Hukumar yaki da cin hanci da ana yiwa tattalin arziki zagon kasa (EFCC) na binciken batar kudaden a hannun sa ba tun yau ba, kuma har ma an gurfanar da shi a kotu.
Ana zargin Gamawa ne tare da wasu mutane biyar a Bauchi da zargin karbar naira miliyan 500 na kudin kamfen a cikin 2015 lokaciniuuftufgyuu
ya na PDP.
gariyawaye
Wednesday, 9 January 2019
Da dumi dumi: An gano badakalar N500m da ake zargin Gamawa da hannu a ciki dumu-dumu
Hukumar yaki da cin hanci da ana yiwa tattalin arziki zagon kasa (EFCC) na binciken batar kudaden a hannun sa ba tun yau ba, kuma har ma an gurfanar da shi a kotu.
Ana zargin Gamawa ne tare da wasu mutane biyar a Bauchi da zargin karbar naira miliyan 500 na kudin kamfen a cikin 2015 lokacin ya na PDP.
Ana zargin Gamawa ne tare da wasu mutane biyar a Bauchi da zargin karbar naira miliyan 500 na kudin kamfen a cikin 2015 lokacin ya na PDP.
Thursday, 18 January 2018
Thursday, 13 October 2016
Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Sakin 21 Daga Cikin 'Yan Matan Chibok
Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Sakin 21 Daga Cikin 'Yan Matan Chibok
Ga Abinda Kakakin Shugaban Kasa Malam Garba Shehu Ya Ce:
"Ta tabbata an saki 21 daga cikin 'yan matan Chibok kuma yanzu haka suna tare da hukumar DSS.
"A dazun nan Babban Daraktan hukumar ta DSS Malam Lawal Daura ya gama yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari bayani kan batun.
"Sako yaran ba ya rasa na saba da tattaunawar da gwamnatin tarayya take da kungiyar Boko Haram din da taimakon kingiyar agaji ta duniya da kuma gwamnatin kasar Switzaland. Kuma za a ci gaba da tattaunawar.
Shugaban kasa ya ji dadin sakin yaran.
Yanzu haka shugaban DSS, Malam Lawal Daura yana bukatar yaran su samu hutu sabida sun gaji, kafin daga bisani a mika su ga mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo. Saboda shugaba Buhari zai haura kasar Jamus an jima.
Za a kuma a bayyana sunayen wadanda aka sako din nan bada jimawa ba.
Wednesday, 24 August 2016
Wasu ‘yan bindiga da har zuwa yanzu ba a san ko su wanene ba sun sace Honarabul Ibrahim Ismail Dan Majalisar Jihar Kaduna mai Wakiktar Tudun Wada. An dai sace Dan majalisar ne a safiyar jiya Talata, inda masu garkuwan sukai awan gaba da shi akan hanyarsa don ziyartar dan uwansa a yankin Abakwa. Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna Aliyu Usman ya tabbatar da aukuwar lamarin yayin da ya bayyanawa manema labarai cewa, yanzu haka hukumar na bnciken lamarin.
Hukumar ‘yan sandan jihar Ogun sun cigaba da tsare Joe Fortomose Chinakwe wanda ya sanyawa karensa suna Buhari a kurkuku.
Rundunar ‘yan sandan jihar ce dai ta gurfanar da Joe Fortomose Chinakwe a gaban kotun majistare a jiya Litinin, bisa zargin shirin tada zaune tsaye, sakamakon yawon da yake yi da karen sa, wanda ya rubuta sunan Buhari a sassan jikin karen.
Jim kadan, kotun dai ta bada belinsa, to sai dai bai cika sharudan beli ba, dan haka aka ci gaba da tsare shi a gidan kaso.
Yan Bindiga Sun Sace Wani Dan Majalisar Jihar Kaduna
Wasu ‘yan bindiga da har zuwa yanzu ba a san ko su wanene ba sun sace Honarabul Ibrahim Ismail Dan Majalisar Jihar Kaduna mai Wakiktar Tudun Wada.
An dai sace Dan majalisar ne a safiyar jiya Talata, inda masu garkuwan sukai awan gaba da shi akan hanyarsa don ziyartar dan uwansa a yankin Abakwa.
Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna Aliyu Usman ya tabbatar da aukuwar lamarin yayin da ya bayyanawa manema labarai cewa, yanzu haka hukumar na bnciken lamarin.
CBN Ta Dakatar Da Bankuna Tara Daga Hada-Hadar Kudaden Waje
Babban bankin Najeriya, CBN ya dakatar da wasu bankuna tara hada-hada da kudaden kasashen waje saboda kin sanya fiye da dala biliyan biyu na kamfanin mai na kasar, a asusun bai daya na gwamnati kamar yadda aka tsara.
Sai dai Babban bankin Najeriya, CBN bai fito a hukumance ya bayyana hakan ba, amma an dauki matakin ne bayan korafin da kamfanin na NNPC ya kai ga gwamnatin tarayya.
Bayanai sun nuna cewa sabon shugaban NNPC, Dokta Maikanti Kacalla Baru ya bukaci gwamnatin ta taimaka wajen ganin bankunan sun sanya kudaden a lalitar gwamnati.
Bankunan da lamarin ya shafa sun hada da: First Bank, UBA, First City Monument Bank, Diamond Bank, Fidelity Bank, Heritage Bank, Sterling Bank, Key stone Bank da kuma Sky Bank.
Gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ta bullo da tsarin asusun bai daya, wadda dukkan hukumomi da ma’aikatun gwamnati za su dinga zuba kudade.
Subscribe to:
Comments (Atom)