Wednesday, 24 August 2016

Yan Bindiga Sun Sace Wani Dan Majalisar Jihar Kaduna








Wasu ‘yan bindiga da har zuwa yanzu ba a san ko su wanene ba sun sace Honarabul Ibrahim Ismail Dan Majalisar Jihar Kaduna mai Wakiktar Tudun Wada.

An dai sace Dan majalisar ne a safiyar jiya Talata, inda masu garkuwan sukai awan gaba da shi akan hanyarsa don ziyartar dan uwansa a yankin Abakwa.

Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna Aliyu Usman ya tabbatar da aukuwar lamarin yayin da ya bayyanawa manema labarai cewa, yanzu haka hukumar na bnciken lamarin.

No comments:

Post a Comment